Connect with us

News

Ku mayar wa ‘yan kasuwa kayan abinci da kuka ƙwace, umarnin Tinubu ga Hukumar Kwastom

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Shugaban Hukumar Kwastam, Bashir Adeniyi ya bayyana cewa shugaban ƙasa Bola Tinubu ya umarci hukumar ta mayar da duka abincin da ta ƙwace daga wajen mutane a iyakokin Najeriya domin siyar da su a kasuwannin kasar nan.

Cikin wata sanarwa da hukumar Kwastam ɗin ta fitar a shafinta na X, ta ce Adeniyi ya bayyana hakan ne lokacin wata ziyara da ya kai iyakar Kwangwalam da ke ƙaramar hukumar Mai’adua a jihar Katsina inda ya gana da masu ruwa da tsaki ranar Asabar.

Mata Za Su Iya Magance Matsalar Najeriya Idan Aka Basu Tarbiya Mai Kyau Da Kuma Ilimi —Malam Ibrahim Khalil

Adeniyi ya ce Tinubu ya yi haka domin kawo sauki ga al’ummar Najeriya duk da cewa doka ta bada dama a kwace kayan kuma kada a maida wa masu fasakwuari kayansu.

Ya ce za a saka ido a tabbatar an dawo da abincin cikin gida kuma an siyar da su ga al’umman Najeriya cikin sauki.

Idan ba a manta ba, Jami’an kwastam sun kama motocin kaya sama da 22 a makon jiya cike makil da buhunan kayan abincin za a fice kasar nan da su.

Advertisement

Sai dai kuma Tinubu ya umarci da a maida wa masu shi da dukka waɗanda aka kama a baya, amma fa da sharaɗin ,a su saida su a kasuwannin Najeriya.

 

 

 

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending