News
Yanzu-Yanzu: An Ga Watan Ramadan A Saudiyya
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Rahotanni daga Kasar Saudiyya sun tabbatar da ganin jinjirin watan azumin Ramadan na bana a sassa daban-daban na kasar a ranar Lahadi.
Hakan dai na nufin ranar Litinin ce, za ta kasance daya ga watan Ramadan na shekarar 1445 bayan Hijira, wacce ta yi daidai da 11 ga watan Maris 2024.
Azumi: Hukumar Tace Fina-finai Ta Bada Umarnin Kulle Gidajen Galar Dake Fadin Jahar Kano
Hakan na zuwa ne bayan watan Sha’aban ya cika kwana 29, inda dama watannin Musulunci ba sa wuce kwana 29 zuwa 30.
Al’ummar Musulmai a fadin duniya dai kan azumci tsawon Ramadan, wanda shi ne wata na tara a kalandar Musulunci, inda suke kauracewa ci da sha da kuma saduwa da iyali tun daga fitowar rana har zuwa faduwarta.
Kazalika, azumi na daya daga cikin shika-shikan addinin Musulunci guda biyar.
A halin yanzu dai a Najeriya ana jiran dakon sanarwa daga Fadar Sarkin Musulumi, Muhammad Sa’ad Abubakar III, game da ganin watan na Ramadan.
-
News3 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion6 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News3 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
