Connect with us

News

Gwamnatin Tarayya Ta Tsawaita Ranakun Hutun Karamar Sallah

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Gwamnatin Tarayya ta amince da sanya Alhamis, 11 ga watan Afrilun 2024 a cikin jerin kwanakin hutun karamar sallah da ta bayar.

Advertisement

Hakan dai na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Ministan Harkokin Cikin Gida, Dokta Olubunmi Tunji-Ojo ya fitar a safiyar wannan Talatar.

Yadda Matsalar Ruwan Sha Ta Addabi Kanawa

Wannan na zuwa ne sakamakon rashin ganin jinjirin watan Shawwal a jiya Litinin da zai kawo ƙarshen watan Ramadan.

Advertisement

Sanarwar mai ɗauke da sa hannun Babbar Sakatariya a Ma’ikatar Harkokin Cikin Gida, Dokta Aishetu Gogo Ndayako, tana kuma taya al’ummar Musulmi kammala Azumin watan Ramadana lafiya tare da fatan Allah Ya karɓi ibadu.

Aminiya ta ruwaito cewa, a ranar Lahadin da ta gabata ce Gwamnatin Tarayya ta ayyana wannan Talatar da gobe Laraba a matsayin ranakun hutun sallah karama a faɗin Najeriya.

Advertisement

Sai dai kuma a sakamakon rashin ganin watan Shawwal ne Majalisar Ƙolin Musulunci ta Nijeriya ta ayyana Laraba a matsayin ranar bikin sallah.

Gwamnatin Tarayya dai ta saba bayar da kwanaki biyu ne a matsayin ranakun hutun sallah domin ma’aikata da sauran al’ummar ƙasar.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending