News
Almajirai Shida Sun Rasu Sakamakon Kamuwa Da Cutar Sankarau.
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Almajirai shida a makarantar Islamiyya ta Tsangaya da ke garin Udobo a karamar hukumar Gamawa a jihar Bauchi sun rasu sakamakon kamuwa da cutar sankarau.
A cewar shugaban riko na karamar hukumar Gamawa, Nairu Baukura, yace wasu almajirai biyu daga makarantun Tsangaya suna karbar magani a asibitin Udobo yanzu haka.
Kamfanoni Ne Ya Kamata Su Biya Harajin Tsaron Intanet Ba Mutane Ba
Yayin da Baukura ya kasa tabbatar da adadin mutanen da abin ya shafa, ya bayyana cewa wasu dama sunyi jinya kuma an sallame su.
Channels ta ruwaito cewa barkewar cutar ta bazu a cibiyoyin Tsangaya guda uku da ke cikin karamar hukumar.
Dangane da lamarin, Shugaban Hukumar Kula da Lafiya a matakin farko ta Jihar Bauchi, Rilwanu Mohammed, ya tabbatar da cewa jihar na kokarin shawo kan cutar.
Ya bayyana cewa kananan hukumomi bakwai sun samu rahoton bullar cutar sankarau.
Mohammed ya bayyana cewa majinyatan da suka yi mu’amala da wadanda abin ya shafa ana ba su magunguna don hana yaduwar cutar.
Sai dai ya ce jihar ta samu damar yi wa mutane allurar rigakafi a kananan hukumomi biyu kawo yanzu.
Jami’in kiwon lafiyar ya yi gargadin cewa ana kamuwa da cutar ta hanyar tarurrukan jama’a, yana mai jaddada muhimmancin matakan kariya don dakile barkewar cutar.
