Sports
A Yau Za’a Buga Wasan Karshe Na Kofin Zakarun Nahiyar Turai
DAGA UMAR IBRAHIM HOTORO
Za’a fafata wasan ne tsakanin kungiyar kwallon kafa ta Real madrid ta kasar andulus da kungiyar kwallon kafa ta Borusia Dortmond ta kasar Jamus.
Wasan zai wakana a babban filin wasa na kasa da kasa na kasar Ingila wato Wembley, karkashin jagorancin alkallin wasa slavko vincic dan asalin kasar Slovenia da misalin karfe 8 na dare.
Wannn shi ne karon farko Real Madrid da Borussia Dortmund za su kara a wasan karshe a babbar gasar tamaula ta Turai, amma karo na 15 da za su fuskanci juna a gasar.
Real madrid ce kan gaba da jumullar kofina 14 yayinda Dortmond take da guda 1 amma tana fatan lashe na 2 a tarihi. musamman la’akari da tayi wajen doke madrid da ci 4 da nema ta hannun tsohon dan wasanta Robert Lewendoski.
Ƙungiyar da Edin Terzic ke jan ragama ta kai wannan matakin, bayan da ta kai zagaye na biyu daga rukuni na shida, sannan ta fitar da PSV a zagayen ƴan 16.
Haka kuma Dortmund ce ta yi waje da Atletico Madrid a zagayen quarter-finals, sannan ta yi nasara a daf da karshe a kan Paris St Germain gida da waje.
Ƙungiyar Dortmond ta kai zagaye na biyu daga rukuni na shida, sannan ta fitar da PSV a zagayen ƴan 16, kuma ta yi waje da Atletico Madrid a zagayen daf dana karshe sannan ta yi nasara a wasan kusa dana karshe a kan Paris St Germain gida da waje.
Itama kungiyar ta Real madrid tayi nasara akan manyan kungiyoyi wadanda suka hada da kungiyar manchester city a wasan kusa dana karshe sannan ta doke Bayern munich a wasan daf dana karshe.
Shin menene ra’ayinku dangane da wannan babban wasa?
