News
Da Dumi Dumi: Shugaba Tinubu Ya Ƙirƙiro Sabuwar Ma’aikata
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya kafa sabuwar Ma’aikatar Harkar Kiwon Dabbobi.
Ya sanar da hakan ne lokacin da ya ƙaddamar da kwamitin da zai gyara tsarin kiwo.
Majalisar Wakilai Ta Yi Watsi Da Yarjejeniyar SAMOA Da Gwamnatin Tarayya Ta Rattaba Hannu A Kai
Kwamitin zai yi aiki wajen magance matsaloli tsakanin manoma da makiyaya.
A taron, mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima, sakataren Gwamnatin Tarayya, George Akume da shugaban ma’aikatan fadar shugaban ƙasa, Femi Gbajabiamila, da wasu jami’an gwamnati na daga cikin waɗanda suka halarci taron.
A watan Satumban 2023, Shugaba Tinubu ya amince da kafa kwamitin shugaban ƙasa don gyaran ɓangaren kiwo da magance rikice-rikicen makiyaya da manoma.
Wannan shawarar ta biyo bayan rahoton taron ƙasa kan gyara tsarin kiwo da rage rikice-rikicen da ke da nasaba da kiwo a Najeriya.
Kungiyar Miyetti Allah ta MACBAN, ta buƙace shugaban ƙasa ya ƙirƙiro ma’aikatar kiwo.
Shugabansu, Alhaji Baba Usman Ngelzarma, ya ce makiyaya na buƙatar ma’aikata mai zaman kanta da za ta kula da dukkanin al’amuran da suka shafi kiwo.
Ngelzarma ya bayyana cewa samun ma’aikatar zai magance dukkanin sarƙaƙiyar da ta shafi kiwo, kamar kasuwanci, sufuri da tsaro, maimakon mai da hankali kawai kan kiwo.
-
News5 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News1 day ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News6 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
