News
Kaduna, Nasarawa, Zamfara Da Wasu Jihohi 10 Na Fuskantar Barazanar Ambaliyar Ruwa —NiMet
Hukumar Kula da Yanayi ta Nijeriya (NiMet) ta yi gargaɗin yiwuwar samun ambaliyar ruwa ta ba-zata a jihohi 13 daga ranar 11 zuwa 20 ga Agustan 2026.
NiMet ta fitar da gargaɗin ne a wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na X a ranar Talata, inda ta lissafa Sokoto, Zamfara, Kebbi, Neja, Kaduna, Nasarawa, Adamawa, Filato, Benue, Kogi, Taraba, Cross River da Akwa Ibom a matsayin jihohin da ke cikin babban haɗarin fuskantar ambaliyar ruwa.
Wani Matashi Mai Shekaru 18 Ya Rasa Ransa Bayan Fadawa Cikin Ruwa A Kano
Hukumar ta ce hasashen ya dogara ne kan yawan ruwan sama da ake sa ran za a samu, danshin ƙasa, ƙarfin magudanan ruwa, yanayin ƙasa da kuma yanayin madatsun ruwa.
Ta ce manufar wannan gargaɗi ita ce taimakawa wajen shiryawa tun da wuri, ɗaukar matakan gaggawa da rage haɗarin bala’o’i.
NiMet ta yi gargaɗin cewa ambaliyar ruwa ta ba-zata na iya faruwa a yankunan da ambaliyar ruwa ta fi yawan faruwa, wuraren da suke ƙasa, birane da kuma al’ummomin da ke kusa da koguna. Hakan na iya haifar da rufe hanyoyi, cunkoson ababen hawa da kuma kawo cikas ga harkokin sufuri.
Hukumar ta kuma yi gargadin cewa ambaliyar ruwa na iya dakatar da samar da wutar lantarki da ayyukan sadarwa na ɗan lokaci, yayin da ruwan sama mai ƙarfi zai iya rage gani ga direbobi tare da shafar zirga-zirgar ababen hawa da harkokin sufurin jiragen sama.
A cewar hukumar, taruwar ruwa a ƙasa na iya lalata gonaki, amfanin gona da dabbobi, yayin da ambaliyar ruwa ta ba-zata za ta iya lalata hanyoyi, gadoji, magudanan ruwa da sauran muhimman ababen more rayuwa.
NiMet ta ƙara da cewa idan aka yi ambaliyar, ruwan da ke tsayawa kan ƙara haɗarin yaɗuwar cututtukan da ruwa ke ɗauka.
Hukumar ta shawarci mazauna yankunan da abin ya shafa da su riƙa bibiyar hasashen yanayi da sanarwar gargadin ambaliya daga NiMet da hukumomin kula da bala’o’i.
Ta kuma yi kira ga jama’a da su guji tafiya ko tuƙi a kan hanyoyin da ambaliyar ruwa ta mamaye, gadoji da wuraren da ruwa ke gudana da ƙarfi.
Ta shawarci mutanen da ke zaune a wuraren da ke cikin haɗari da su kasance cikin shiri, tare da kasancewa a shirye sannan su yi ƙaura zuwa wuraren da suka fi aminci idan buƙatar hakan ta taso.
Hukumar ta kuma buƙaci hukumomin kula da bala’o’i da su ƙarfafa sa ido, shirya tawagogin ɗaukar matakin gaggawa tun da wuri, tare da tabbatar da kasancewa cikin shiri ko da yaushe.
Ga manoma kuwa, NiMet ta shawarce su da su inganta magudanan ruwa a gonakinsu, tare da kwashe dabbobi, injinan noma da amfanin gonar da aka girbe zuwa wuraren da ba sa fuskantar haɗarin ambaliya.
-
News1 day ago
Ba Za Mu Yi Wa Kowa Rangwame Ba A Wajan Yaƙi Da Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi Ba — Muhyi Magaji
-
News2 days ago
Ana Zargin Matar Aure Da Shaƙe ’Yar Kishiyarta Mai Shekara 3 Har Lahira
-
News6 days ago
KANO: Yara 24 Da Ake Tuhuma Da Laifi Sun Amfana Da Shirin Gyaran Tarbiya Maimakon Hukuncin Kotu A Watan Yuli
