Connect with us

News

Jami’an DSS Sun Cafke Waɗanda Suka Yi Garkuwa Da Mahaifiyar Rarara A Dajin Maƙarfi

Published

on

DAGA MUHAMMAD BASHIR MUSA 

Jami’an Hukumar tsaro ta DSS a Kano sun kama ɗaya daga cikin waɗanda suka shirya sace mahaifiyar fitaccen mawakin siyasa, Dauda Kahutu Rarara. Yayin artabun guda daga cikin masu garkuwar ya mutu wani wanda ake zargi da kuma samun kudi har ₦26.5 miliyan.

Advertisement

Wani babban jami’i a hukumar DSS ya bayyana cewa, tawagar musamman ta DSS, bisa ga bayanan sirri masu inganci, sun kama wata tawaga ta ‘yan bindiga biyar a dajin Maƙarfi yayin da suke raba kuɗin fansa. An kama ɗaya daga cikin su, Hamisu Tukur, da raunin harbin bindiga, yayin da aka kashe wani wanda ake zargi, Bature.

Babban bankin Najeriya CBN ya umarci bankuna su tura kudaden asusun da suka daina aiki

Lamarin sacewar ya faru ne makonni uku da suka gabata lokacin da wasu ‘yan bindiga suka shiga gidan Hajiya Hauwa’u Adamu, mahaifiyar Rarara, a Kahutu, suka yi garkuwa da ita.

Advertisement

Ta samu ‘yancinta bayan ta shafe kwanaki 20 a hannun masu garkuwa.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending