News
Ya Zama Dole Gwamnati Ta Samar Wa Matatar Man Dangote Ɗanyan Man Da Za Tayi Amfani – Ƙungiyar lauyoyin Najeriya
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Ƙungiyar lauyoyin Najeriya ta gargadi gwamnatin ƙasar da kar ta kuskura ta bari matatar man dangote ta durƙushe saboda rashin samun ɗanyan man da za tayi amfani da shi wajen gudanar da ayyukanta.
Shugaban ƙungiyar mai barin gado Yakubu Mai Kyau ya ce abin baƙin ciki ne yadda Dangote ke fuskantar zagon ƙasa daga bangarori da dama wajen ganin matatar ta fara aiki gadan gadan.
Yara Fiye Da Miliyan Hudu Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa A Arewacin Najeriya – Gwamnatin Tarayya
Mai Kyau ya zargi masu shigo da mai ƙasar waɗanda suka hana Najeriya tace mai a gida da haifar da tarnakin da ya hana sabuwar matatar aikin tace man da zai hana ƙasar shigo da shi daga ƙasashen ƙetare.
Shugaban wanda ya jagoranci tawagar muƙarrabansa domin ziyarar gani da a ido matatar dake unguwar Lekki a Lagos, ya ce abinda ya gani ya faranta masa rai matuka, yayin da ya bayyana Aliko Dangote a matsayin mai fafutukar ƴantar da jama’a kuma gwarzo saboda sadaukar da ran da ya yi wajen zuba jarin dala biliyan 20 domin samar da matatar.
Mai Kyau ya buƙaci gwamnatin Najeriya ta gaggauta samar da yanayi mai kyau ta yadda wannan matatar zata fara aiki gadan gadan domin ragewa Najeriya wahalar da ta ke sha na samun tacaccen man.
-
News2 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion6 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News2 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
