Connect with us

News

Mahalarta Ɗaurin Aure 19 Daga Kano Sun Kone Kurmus A Hatsarin Mota A Filato

Published

on

Yan daurin aure 19 daga Kano sun kone kurmus a hatsarin mota a Filato

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN 

Mahalarta ɗaurin aure mutum 19 daga Jihar Kano sun ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota a yankin Kwanar Maciji da ke Ƙaramar Hukumar Pankshin a Jihar Filato.

Advertisement

Mutum 11 daga cikinsu sun tsallaka rijiya da baya da raunuka a haɗarin da ya ritsa da su a yayin da suke hanyar komawa gida bayan ɗaurin auren da aka gudanar a Ƙaramar Hukumar Barikin Ladi a ranar Asabar kamar yanda Jaridar AMINIYA ta ruwaito

Jami’an Hukumar EFCC Sun Kama Ma’aikatan Haraji 5 Bisa Zargin Wawure Naira Biliyan 1.2 A Katsina 

Shugaban Ƙaramar Hukumar Pankshin, John Dasar, ya bayyana cewa motar matafiyan ta kama da wuta ne, amma an yi nasarar ceto direban da wasu fasinjoji.

Advertisement

Ya ce, “an ceto mutane 11 amma mutane 19 sun kone ƙurmus ba za a iya gane su ba, saboda bayan mutane sun zo ana ƙoƙarin ceto fasinjojin ne motar ta kama da wuta, ta cinye ragowar.”

Ya ce an kai waɗanda suka tsira Babban Asibitin Pankshin inda ake duba lafiyarsu.

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending