Connect with us

News

Za a Ci Tarar N25,000 Ga Duk Wanda Aka Kama Yana Tofar da Yawu, Majina, Bahaya Ko Zubar Da Shara A Kano

Published

on

DAGA NUSAIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA 

Majalisar Dokokin Jihar Kano ta amince da wata doka da ke tanadin ci tarar Naira dubu 25 ga duk wanda aka kama yana tofar da yawu, majina, yin bahaya ko zubar da shara a tituna, shagunan kasuwanci, karkashin gadoji da sauran wuraren taruwar jama’a a fadin jihar.

Advertisement

Sabuwar dokar ta biyo bayan matakin da majalisar ta dauka na samar da ingantaccen tsari don kare lafiyar jama’a da kuma kyautata tsaftar muhalli a birnin Kano.

Gwamnatin Tarayya Ta Karyata Jita-jitar Karin Farashin Wutar Lantarki

Wannan doka za ta taimaka wajen tabbatar da aiwatar da ayyukan Hukumar Kawata Birnin Kano da Kula da Wuraren Shakatawa, wadda ke da alhakin tabbatar da tsaftar birnin da kyautata rayuwar al’umma.

Advertisement

Gwamnatin Kano ta bukaci jama’a da su kiyaye dokokin tsaftar muhalli, domin dakile yaduwar cututtuka da kuma bunkasa kyawun birnin Kano. Hukuma za ta sanya ido don tabbatar da bin wannan doka, tare da daukar matakin hukunta duk wanda aka samu da saba wa ka’idojin da aka gindaya.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending