Connect with us

News

Hukumar Kula da Lafiya A Matakin Farko Ta Sabunta Asibitoci 58 A Jihar Nasarawa

Published

on

IMG 20250320 WA0034

DAGA ZUBAIRU M. LAWAL, LAFIA

Gwamnatin Jihar Nasarawa ta fara aikin sabunta asibitoci 58 a fadin jihar ta hannun Hukumar Cigaban Kula da Lafiya ta Firamari (NAPHDA), domin inganta lafiyar al’umma.

Advertisement

Shugaban hukumar, Dr. Usman Saleh, ya bayyana hakan yayin wata zantawa da manema labarai a Lafia, inda ya ce wannan aiki yana da nufin samar da ingantacciyar kiwon lafiya ga kowa. Ya bayyana cewa Bankin Duniya da wasu abokan hulda ne ke tallafa wa shirin, wanda zai inganta kayayyakin aiki da gine-ginen asibitocin da aka zaba.

NYSC Ta Sanar Da Sabuwar Ranar Fara Biyan Alawus N77,000

Dr. Saleh ya ce ana sa ran kammala aikin kafin karshen watan Yuni 2025, yana mai yabawa Gwamna Abdullahi Sule bisa jajircewarsa wajen bunkasa lafiyar jama’a.

Advertisement

Ya bukaci hadin gwiwa da masu ruwa da tsaki, musamman manema labarai, domin wayar da kan jama’a game da muhimmancin kiwon lafiya.

Shugaban Kungiyar Manema Labarai na Jihar, Kwamared Isaac Ukpoju, ya jaddada goyon bayan su ga wannan shiri domin tabbatar da ingantaccen kulawar lafiya a jihar.

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending