Connect with us

News

Adadin Mutanen Da Suka Rasa Rayukansu Sanadiyyar Ambaliyar Ruwa A  Adamawa Ya Karu Zuwa 23

Published

on

Ambaliya a Neja Mutum 110 sun mutu, ruwa ya rushe gidaje fiye da 50 a Mokwa

Adadin mutanen da suka rasa rayukansu sanadiyyar ambaliyar ruwa a wasu sassan jihar Adamawa ya karu zuwa 23.

Gwamnan jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri, ne ya bayyana hakan ranar Litinin yayin da ya kai ziyarar jaje ga iyalan waɗanda suka rasu a ibtila’in da ya auku a ranar Lahadi.

Advertisement

Jami’an Tsaro Sama da 130 Sun Rasa Rayukansu A Katsina

Gwamnan ya nuna damuwarsa da alhini matuƙa bayan ganawa da waɗanda ambaliyar ta rutsa da su, yana mai cewa irin wannan al’amari mai muni bai taɓa faruwa ba a baya ba.

Ambaliyar ta faru ne da misalin ƙarfe 1 na safiyar Lahadi a sakamakon ruwan sama mai yawa da aka yi, wanda ya haddasa mutuwar mutane 23 da kuma lalata dukiyoyi da darajarsu ta kai miliyoyin naira.

Advertisement

Yayin jawabi ga waɗanda abin ya shafa a sansanin wucin gadi da aka kafa a Kwalejin Aliyu Mustafa, Yola, Gwamna Fintiri ya sanar da kafa kwamitin na musamman don tantance adadin asarar da aka yi.

Ya bayyana halin da aka shiga mara daɗi, inda ya jajanta wa iyalan waɗanda suka mutu da waɗanda suka yi asarar dukiyoyi, yana mai tabbatar da cewa gwamnati za ta tallafa musu wajen sake gina musu gidajen su da sauya muhallinsu.

Advertisement

Fintiri ya kuma soki waɗanda ke yaɗa rahotannin ƙaryar game da lamarin, ba tare da fahimtar ainihin abin da ke faruwa ba, inda ya ce hakan yana da nasaba da tuggun siyasa da son zuciya.

Ya bayyana cewa maƙasudin ambaliyar sun haɗa da ruwan sama mai yawa da toshewar hanyoyin ruwa.

Advertisement

 

 

Advertisement

LEADSHIP

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending