Connect with us

News

An Buƙaci Kotu Ta Hana Jonathan Tsayawa Takara A 2027

Published

on

Ba mu nemi Jonathan don yi mana takara a 2027 Jam'iyyar PDP

Wata babbar kotun tarayya da ke zaune a Abuja, ta samu buƙatar dakatar da tsohon shugaban ƙasa, Goodluck Jonathan, daga tsayawa takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2027 ko kowanne zaɓen shugaban ƙasa nan gaba.

Wannan buƙata ta fito ne daga wani lauya, Johnmary Jideobi, wanda ya shigar da ƙara gaban kotun. A cikin ƙarar, mai ƙarar ya nemi a hana Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Najeriya (INEC) karɓa ko wallafa sunan Jonathan a matsayin ɗan takara.

Advertisement

Majalisar Wakilai Ta Kafa Kwamiti Don Duba Harkokin Kuɗin Kirifto Da POS A Najeriya

Mai ƙarar ya bayyana cewa Jonathan ya kammala wa’adin mulki biyu da Kundin Tsarin Mulki ya tanadar: na farko bayan wafatin marigayi shugaban ƙasa Umaru Musa Yar’Adua, sannan na biyu bayan nasarar da ya samu a zaɓen 2011.

Duk da buƙatar da aka shigar, kotun ba ta sanya ranar fara sauraron ƙarar batukuna.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending