News
Majalisar Wakilai Ta Kafa Kwamiti Don Duba Harkokin Kuɗin Kirifto Da POS A Najeriya
Majalisar Wakilai ta Najeriya ta kafa wani kwamiti na musamman domin duba yadda ake amfani da kuɗaɗen kirifto da kuma na’urorin POS, wadanda ke ƙara tasiri a harkokin tattalin arziƙi, tsaro da kuɗi a ƙasar.
Kakakin majalisar, Abbas Tajudeen, ya ce matakin ya zama dole ne saboda yawaitar damfara, laifukan yanar gizo, da amfani da kuɗin intanet wajen aikata miyagun ayyuka, waɗanda ke zama barazana ga tsaron ƙasa da tattalin arziƙi.
Ya ce duk da cewa kirifto na iya taka muhimmiyar rawa wajen bunƙasa tattalin arziƙin ƙasa, akwai kuma haɗarin da ke tattare da shi, musamman wajen safarar kuɗaɗen haram, ta’addanci, da rashin tsari a fannin doka.
“Kwamitin zai tsara sabbin dokoki da za su taimaka wajen daidaita harkar da kare masu amfani da wannan sabuwar fasahar kuɗi,” in ji kakakin majalisar.
Shugaban kwamitin, Olufemi Bamisile, ya ce za su yi aiki tare da hukumomin gwamnati irin su Babban Bankin Najeriya (CBN), Hukumar Tsaro ta Kuɗi (SEC), EFCC da kuma ‘yan sanda, domin tabbatar da cewa ci gaban fasahar kuɗi bai zama barazana ga tsaron ƙasa ba.
Ya ƙara da cewa kwamitin zai gudanar da zaman jin ra’ayoyi daga masana da masu ruwa da tsaki kafin ya kammala rahotonsa, wanda za a gabatar wa majalisar domin ɗaukar mataki.
