News
Matashiya Mai Koyon Tuƙi Ta Murƙushe Yara Uku ’Yan Gida Ɗaya
Wata matashiya da ke koyon tuƙi ta murƙushe wasu yara uku ’yan gida ɗaya bayan da mota ta kutsa cikin gidansu a yankin Ogbunabali da ke birnin Fatakwal na Jihar Ribas.
Rahotanni sun bayyana cewa hatsarin ya faru ne yayin da wani saurayi ke koyar da budurwarsa tuƙi, inda a wani lokaci ta rasa yadda za ta sarrafa motar, lamarin da ya sa motar ta afka cikin gidan da yaran ke ciki.
An Kama Wata ‘Yar TikTok Da Ke Barazana Ga Rayuwar Shugaban Kasa
Yaran da hatsarin ya rutsa da su na da shekaru 10, 4 da kuma 3, kuma rahotanni sun ce sun mutu nan take sakamakon mummunan hatsarin.
Wata majiya daga yankin ta shaida cewa aukuwar lamarin ta tayar da hankali matuƙa a unguwar, yayin da mahaifiyar yaran ta shiga cikin matsanancin alhini tana neman a yi mata adalci.
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Ribas ta tabbatar da faruwar lamarin, tana mai cewa an kaddamar da bincike domin gano cikakken musabbabin hatsarin.
Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, Olugbenga Adepoju, ya bayyana jimaminsa kan lamarin, inda ya tabbatar da cewa za a bi diddigin lamarin dalla-dalla tare da hukunta duk wanda bincike ya nuna yana da hannu a aukuwar hatsarin.
Har ila yau, rundunar ta bukaci jama’a da su kwantar da hankalinsu tare da bai wa jami’an tsaro cikakken haɗin kai yayin gudanar da bincike.
-
News3 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion6 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News3 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
