News
Za a gudanar da addu’o’in cika shekara da rasuwar Buhari a ranar Litinin
Tsohon mai taimaka wa tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari kan harkokin yaɗa labarai, Bashir Ahmad, ya sanar da shirin gudanar da addu’o’i da taron tunawa da cika shekara ɗaya da rasuwar tsohon shugaban ƙasar.
A cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X, Bashir Ahmad ya ce za a gudanar da taron ne a ranar Litinin, 13 ga Yulin 2026, domin tunawa da rayuwa, gudunmawa da kuma hidimar da Buhari ya yi wa Najeriya.
Jami’an Ƴansanda Sun Kama Mahaifin Prince Adeyemi Adeniyi, Mutumin Da Ake Zargi Da Kafa Hukumar Bogi
Ya bayyana Buhari a matsayin shugaba mai jajircewa, gaskiya, ɗa’a da kishin ƙasa, yana mai cewa irin gudunmawar da ya bayar wajen ci gaban Najeriya za ta ci gaba da kasancewa cikin tarihi.
A cewarsa, yan uwa, abokai, tsoffin hadimai, abokan siyasa da sauran yan Najeriya za su hallara domin yin addu’o’i tare da roƙon Allah Ya gafarta wa marigayin kura-kuransa, Ya sa Aljannar Firdausi ta zama makomarsa, sannan Ya ba iyalansa da al’ummar Najeriya haƙurin rashinsa.
Marigayi Muhammadu Buhari ya rasu ne a ranar 13 ga Yulin 2025 yana da shekaru 82, bayan fama da jinya a wani asibiti da ke birnin London na ƙasar Birtaniya.
Daga bisani aka dawo da gawarsa Najeriya, inda aka yi masa jana’iza a garinsu na Daura a Jihar Katsina.
-
News4 days ago
Hukumar Kula Da Harkokin Shari’a Ta Tilasta Wa Alƙali Ritaya Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Naira 250,000 A Kano
-
News5 days ago
Jigawa: Sama da Gine-gine 200 Sun Lalace Sakamakon Iska Da Ruwan Sama Mai Ƙarfi
-
News4 days ago
Wasu Fusatattun Matasa Sun Hallaka Wani Mutum Tare Da Kona Gawarsa Kan Zargin Satar Babur A Kano
