Connect with us

News

Shugaba Tinubu Ya Miƙa Wa Majalisar Dattawa Ƙudirin Gyaran Dokar Ilimin Makarantun Sakandare

Published

on

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya aike wa Majalisar Dattawa da ƙudirin dokar gyaran Hukumar Kula da Manyan Makarantun Sakandare ta Ƙasa (NSSEC) na shekarar 2026, inda ya buƙaci majalisar ta gaggauta amincewa da shi domin inganta yadda ake gudanar da manyan makarantun sakandaren gwamnati a Nijeriya.

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ne ya karanta wasiƙar shugaban ƙasar a zaman majalisar da aka gudanar ranar Alhamis.

Kotu ta Aike da Tsohon Shugaban Kotun Da’ar Ma’aikta Gidan Gyaran Hali Na Kuje

A cikin wasiƙar, Tinubu ya bayyana cewa Majalisar Zartarwa ta Tarayya (FEC) ta amince da ƙudirin a taronta na ranar 30 ga Afrilu, 2026, kafin Ma’aikatar Shari’a ta tantance tare da kammala shirya shi bisa tanadin doka.

Shugaban ƙasar ya ce gyaran dokar wani ɓangare ne na ƙoƙarin gwamnatinsa na ƙarfafa cibiyoyin ilimi da kuma inganta tsarin tafiyar da manyan makarantun sakandare na gwamnati.

Ya kuma roƙi Majalisar Dokoki ta Ƙasa da ta yi nazari tare da amincewa da ƙudirin cikin gaggawa, yana mai cewa hakan zai taimaka wajen inganta shugabanci da gudanar da manyan makarantun sakandare a faɗin ƙasar.

Advertisement

Ana sa ran ƙudirin zai taimaka wajen ci gaba da sauye-sauyen da Gwamnatin Tarayya ke aiwatarwa domin inganta tsarin ilimin sakandare a Nijeriya.

 

 

 

PUNCH

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending