News
Najeriya ba za ta tsoma baki a shari’ar Sanata Ike Ekweremadu
Daga Muhammad Muhammad zahraddin
Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ce ba za ta tsoma baki a shari’ar da ake yi wa tsohon mataimakin shugaban majalisar dattawa Sanata Ike Ekweremadu a birnin Landan na kasar Birtaniya ba.
Babban Lauyan Tarayya kuma Ministan Shari’a, Abubakar Malami, wanda ya bayyana haka ya yi wani taron manema labarai a fadar gwamnati, dake Abuja a ranar Alhamis ya ce gwamnatin Najeriya na da al’adar rashin tsoma baki a duk wani lamari na shari’a na gida ko na waje.
Wannan matsayi, a cewarsa, zai ci gaba da tsayawa kan lamarin da ya shafi tsohon mataimakin shugaban majalisar dattawa, Ike Ekweremadu a shari’ar da ake yi masa a kotun Burtaniya.
Da aka tambaye shi kan matakin da Gwamnatin Tarayya ta yi na sa baki a shari’ar da ta shafi Sanata mai wakiltar Enugu ta Yamma a Majalisar Dokoki ta kasa dangane da shari’ar da ake yi masa a Birtaniya, Malami ya ce, “Bai taba zama al’adar gwamnatin Najeriya ta tsoma baki kan wani abu na shari’a na gida ko na waje. Kuma wannan shine matsayin gwamnati.
