News
Yan bindiga sun yi garkuwa da wasu manyan ‘ya’yan jam’iyar APC a Imo
Daga: Kabiru basiru fulatan
Yan bindiga sun yi garkuwa da wasu mambobin APC biyu da kuma kashe mutum uku a jihar Imo.
Rahotanni na cewa maharan sun kwace ikon babban titin owerri-Okigwe na tsawon sa’o’i suna cin karensu ba babbaka.
Sannan sun yi garkuwa da matafiya da dama. Cikinsu akwai wani da aka bayyana da Mista Aloy Onuekwusi mai kamfanin Diamond Pools.
Cikin wadanda aka kashe har da direban mutanen da aka yi garkuwa da su.
Shaidu sun shaida yada maharan suka haifar da cunkoson ababen hawa sakamakon juyawa da mutane suka rinka yi domin tsira da ransu.
BBC
Advertisements
