Connect with us

News

Yan sanda sun kama ‘sojan boge’ da zargin yi wa mata fashi a Jihar Legas

Published

on

Sojan bogi

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Dakarun bincike na rundunar ‘yan sandan Najeriya reshen Jihar Legas sun kama wani mutum da zargin bayyana kan sa a matsayin soja don aikata fashi da damfarar ‘yan mata.

Advertisement

 

Sojan bogen mai shekara 39 kan bayyana kan sa a matsayin dillalin tallata kayayyaki sannan ya gayyaci mata don gwada basirarsu, amma daga ƙarshe sai ya ƙwace musu kayayyaki ta hanyar ritsa su da bindiga, a cewar sanarwar da rundunar ta fitar ranar Lahadi.

Advertisement

YANZU-YANZU: Atiku ya sauka a Kano domin karɓar Shekarau zuwa PDP

Sanarwar ta ce an kama mutumin bayan ɗaya daga cikin waɗanda ya yi wa fashin ta kai rahoton ƙwace mata mota ƙirar Lexus RX330.

Advertisement

 

Binciken da rundunar ta gudanar ya gano ƙarin motar alfarma da keken ɗinki da na’urar cire kuɗi ta POS a wajensa.

Advertisement

 

Ta nemi masu waɗannan kayayyaki da su gabatar da kansu gare ta don karɓar kayayyakinsu, inda ta ce za ta gurfanar da wanda ake zargin a gaban kotu da zarar an kammala bincike a kansa.

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending