Ghana ta ayyana cewa cutar Marburg da ta bulla kasar a baya bayannan a yanzu ba bu ita bayan an shafe kwanaki 42 ba a samu wanda ya kamu da ita ba.
Tun da farko mahukunta a kasar sun an karar da mutane cewa cutar wadda ta bulla a kasar na da matukar hadari in da ake danganta ta da Ebola, bayan da a watan Yuli aka samu mutum biyu da suka mutu sakamakon kamuwa da cutar.
Sarkin Kano ya naɗa Sheikh Daurawa a matsayin limamin massllacin jami’ar Skyline
Mutum ukun da suka kamu da cutar uba da da da kuma mahaifiyar jaririn dan watanni 14 da haihuwa, biyu sun mutu yayin da mahaifiyar kuma ta warke daga baya kuma aka sake gwada ta aka ga ta kamu da cutar.
An rinka gwada mutane 200 da suka yi mu’amala da mutum ukun akai-akai amma daga bisani aka tabbatar ba su kamu da cutar ba.
Wani babban jami’i a ma’aikatar lafiya ta kasar Dr Patrick Kuma-Aboagye, ya shaida wa manema labari cewa a yanzu ba bu cutar a Ghana.
Daga nan ya gode wa Hukumar Lafiya ta Duniya da ma sauran kungiyoyin da suka taimaka wajen kawar da cutar a kasar.
Wannan ne dai karon farko da aka gano cutar ta Marburg a yammacin Afurka.
A bara an samu mutum guda da ya kamu da cutar a Guinea, to amma daga bisani aka
