Connect with us

News

Mutum goma sun rasu a hatsarin kwale-kwale a jihar Kebbi

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHARADDIN

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

An gano gawarwakin mutum goma da suka rasu a hatsarin kwale-kwale a jihar Kebbi, inda masu aikin ceto na can suna ci gaba da kokarin lalubo wasu mutanen wani jirgin ruwa da ya kife da su a garin Samanaji na Karamar Hukumar Koko-Bese.

Advertisement

 

Jirgin dai yana dauke da fiye da mutum dari, amma an samu nasarar ceto mafi yawa daga ciki.

Advertisement

Kwamishiniya Ta Yi Murabus Bayan An Tube Wa Mahaifinta Rawani

Alhaji Yahaya Bello Koko, wanda ya kasance shugaban Karamar Hukumar Koko Besi, ya tabbatar wa BBC cewa hadarin ya faru ne lokacin da mutanen ke komawa gida daga gona.

 

Advertisement

Ya ce mutane sun cika makil cikin jirgin tare da mata da kuma yara, inda jirgin ya rabe biyu a tsakiyar ruwa kasancewar tsohon jirgi ne.

 

Advertisement

Shugaban karamar hukumar ya ƙara da cewa an ceto mutane fiye da 80, inda aka gano gawarwaki goma, akwai kuma goma har yanzu ana neman su.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending