News
Saudiyya da Amurka sun yi maraba da tsawaita yarjejeniyar Sudan
Amurka da Saudiyya sun yi maraba da tsawaita wa’adin yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin sojojin Sudan da dakarun kar-ta-kwana na RSF da kwana biyar.
A cikin wata sanarwar hadin gwiwa, kasashen biyu masu shiga tsakani a rikicin sun amince cewa yarjejeniyar farko da aka cimma ta kasance ta je-ka-na-yi-ka, to amma duk da haka ta bayar da damar shigar da kayan agaji ga miliyoyin mutane a Sudan din.
Abba Kabir Ya Rushe Shugabannin Hukumar Alhazai Ta Jihar Kano Tare Da Nada Sabbi
Shirin samar da abinci na duniya, ya ce a karon farko ya samu damar aikewa da abinci ga mutanen da suka makale a babban birnin kasar, Khartoum, tun bayan fara yaki a Sudan din.
Rikicin da aka fara tsakanin bangarorin biyu a kan gwagwarmayar kama iko tun wajen mako shida ya tilasta wa jama’a da dama ficewa daga kasar musamman babban birnin sannan ya jefa da dama cikin mawuyacin hali.
