News
Sama da mutane 100 ne suka mutu sakamakon kamuwa da cutar Kwalara a Kasar Sudan
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Ma’aikatar lafiya ta kasar Sudan ta sanar da cewa, barkewar cutar kwalara da zazzabin dengue a kasar Sudan da yaki ya yi sanadiyar mutuwar mutane sama da 100 tun daga watan Agusta.
Ma’aikatar ta ce an samu adadin mutane 1,049 da suka kamu da cutar kwalara, 73 daga cikinsu sun mutu a birnin Khartoum na jihar Al-Jazira da ke kudu da Gedaref a yammacin kasar.
Jam’iyyar APC ba ta da ɗan takarar Gwamna a Jihar Bayelsa –Hukumar INEC
Khartoum na daya daga cikin manyan gurin fadace-fadacen da ake gwabzawa ya mamaye kasar tun watan Afrilu.
Dubban daruruwan mazauna babban birnin Khartoum sun yi gudun hijira zuwa yankunan Gedaref da Al-Jazira da aka kwantar da hankula,
Jihohi tara na Sudan sun sami rahoton bullar cutar zazzabin cizon sauro, inda 49 suka mutu daga jimillar mutane 3,316, in ji ma’aikatar.
Jihar Gedaref, mai makwabtaka da Habasha, ta ba da rahoton mutane 2,152 daga cikin wadanda suka kamu da cutar sannan 33 daga cikin wadanda suka kamu sun mutu.
Tun kafin fadan ya barke a cikin watan Afrilu, tsarin kula da lafiya na Sudan ya yi kokarin shawo kan barkewar cutar da ke tare da damina a kasar da ke farawa a watan Yuni.
Rahoton ma’aikatar lafiya ta ce kashi 70 cikin 100 na asibitocin da ke yankunan da yaki ya daidaita ba sa aiki.
