News
Majalisar Wakilai Ta Ce Ba Zata Zama ‘Yar Amshin Shata Ba
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Sabon kakakin zauren majalisar wakilai ta kasa, Tajudden Abbas ya yi alkawarin cewar zauren majalisar na goma ba zai kasance ‘Dan amshin shata ba.
Ya baiyana haka ne ga wakilan kafafen yada labarai na fadar shugaban kasa dake Abuja, Jim kadan bayan ganawarsa da shugaban kasa, Bola Tinubu, bayan yasha rantsuwar kama aiki a jiya.
Kungiyoyin ASUU Da ASUP Sunce Babu Tabbas Wajen Aiwatar Da Dokar Bada Lamunin Karatu
Ya ce ‘yan majalisar wakilan sun zabi ra’ayinsu a faiyace sabanin rahotannin da wasu kafafen yada labarai suka fitarwa.
Ya kuma yi alkawarin cewar bangaren majalisar zai hada kai da bangaren zartarwa domin samar da cigaban da kasar nan ke muradi, tare kuma da kalubalantar tsare-tsaren da suka ci karo da cigaban kasa.
Shima a nasa jawabin, Shugaban majalisar dattawa Sanata Godswill Akpabio, Ya ce zauren majalisar zai bada cikakken goyon bayansa kan cire tallafin mai da shugaban kasa Tinubu ya yi.
