Connect with us

News

Majalisar Wakilai Ta Ce Ba Zata Zama ‘Yar Amshin Shata Ba

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU  FULATAN

Sabon kakakin zauren majalisar wakilai ta kasa, Tajudden Abbas ya yi alkawarin cewar zauren majalisar na goma ba zai kasance ‘Dan amshin shata ba.

Advertisement

Ya baiyana  haka ne  ga  wakilan kafafen yada labarai na fadar shugaban kasa dake Abuja, Jim kadan bayan ganawarsa da shugaban kasa, Bola Tinubu, bayan  yasha  rantsuwar kama aiki a jiya.

Kungiyoyin ASUU Da ASUP Sunce Babu Tabbas Wajen Aiwatar Da Dokar Bada Lamunin Karatu

Ya  ce  ‘yan majalisar  wakilan sun zabi ra’ayinsu a faiyace sabanin  rahotannin da  wasu kafafen yada  labarai  suka   fitarwa.

Advertisement

Ya  kuma yi alkawarin cewar  bangaren majalisar  zai hada  kai  da  bangaren zartarwa domin samar da cigaban  da kasar  nan ke muradi,  tare  kuma  da  kalubalantar  tsare-tsaren  da  suka  ci karo  da  cigaban kasa.

Shima  a nasa jawabin, Shugaban majalisar dattawa  Sanata Godswill Akpabio,  Ya  ce  zauren majalisar  zai bada cikakken goyon bayansa  kan  cire  tallafin mai da shugaban kasa  Tinubu ya yi.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending