Connect with us

News

Za’a Yiwa ‘Yansanda Masu Bada Hannu Akan Titi Karin Girma

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI

 

Advertisement

Sufeton rundunar ‘yansanda ta kasa Usman Alkali Baba, Ya bada umarnin tantance kwazon jami’an rundunar dake aikin bada hannu akan titina da kula da zirga-zirgar ababen hawa, domin yi masu karin girma zuwa matsayi na gaba.

Wata sanarwa da kakakin rundunar, CSP Olumiyiwa Adejobi ya fitar a jiya,  Ta ce  aikin tantacewar  wani bangare ne  na  yiwa jami’an karin girma.

Advertisement

Kungiyoyin ASUU Da ASUP Sunce Babu Tabbas Wajen Aiwatar Da Dokar Bada Lamunin Karatu

Ya ce  sufeton yansandan na kasa  ya bada umarnin daga  likafar  jami’an  yansandan  masu aikin bada  hannu  da suka dace bisa  la’akari da kwazonsu wajen aiki, da kuma shaidar karatu da suke da shi, zuwa  matsayi na gaba.

Kakakin ‘yansandan na kasa, Ya ce  wannan wani bangare ne na kokarin da rundunar  ta take na samarwa da  jami’an ta  cigaban da ake bukata.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending