News
‘Yan kato da gora sun kama mutanen da ke yin tsire da naman Kare
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Jami’an ‘yan kato da gora ta kungiyar ‘yan bijilente a jihar Bauchi sun kama wasu mutane biyu a jihar wadanda suke yin tsire na sayarwa da naman Kare.
Wannan lamari dai ya faru ne a unguwar Yelwan Kagadama da ke jihar Bauchi.
WATA SHARI’A SAI A LAHIRA: ‘Samun alƙalai nagari sai dace – Akpata
Mutanen wadanda sun dade suna wannan sana’a suna yaudarar mutane da cewa tsiren na naman Akuya ne.
Wakilin Gaskiya Ta Fi Kwabo ya jiyo cewa, za a mika mutanen biyu ga ‘Yan sanda domin ci gaba bincike.
A wani labarin kuma WATA SHARI’A SAI A LAHIRA: ‘Samun alƙalai nagari sai dace – Akpata
Hukumomin Taiwan sun ce jiragen China takwas sun ƙetare iyakar da ta zama mallakinta.
Hakan na faruwa ne kwanaki huɗu bayan tattaunawa kan makomar tsuburin tsakanin shugaba Joe Biden na Amurka da shugaban China Xi Jinping.
Rahotanni sun ce jiragen saman na yi wa jirgin ruwan yaƙi na China rakiya.
A ranar Laraba shugabannin biyu sun shafe awa huɗu suna tattaunawa a birnin California.
Kuma Mr Xi ya shaida wa shugaba Biden cewa batun Taiwan shi ne babban abu mai hatsarin gaske a dangantaka tsakanin China da Amurka.
