Connect with us

News

Dalilin da Yasa Tinubu Ya Kamata Ya Sake Duba Nadin Mukamaan kwamishinonin INEC Da Ya Yi – Jega

Published

on

Tsohon Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), Attahiru Jega

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

Tsohon Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), Attahiru Jega, ya yi kira ga Shugaba Bola Tinubu da ya sake duba nadin kwamishinonin Hukumar Zabe ta RECs.

Jega ya ce kamata ya yi Tinubu ya sake duba nadin nasu saboda damuwar da wasu daga cikin REC din suke haifarwa.

Advertisement

Ka Dakatar da Yin Murna Kamar Ronaldo’ – Dan Wasa Vidal Ya Soki Garnacho

Kimanin wata guda kenan Tinubu ya gabatar da sunayen mutane 10, inda majalisar dattawa ta tabbatar da nadin nasu.

Sai dai ana zargin wasu daga cikin REC da hannu a siyasar bangaranci.

Advertisement

Da yake mayar da martani game da sukar, Jega ya ce rashin bitar nadin nasu yana nuna kuskure.

Da yake gabatar da shirin a Gidan Talabijin na Channels a Shirin Politics Today Yau Litinin, Jega ya ce: “Ina ganin ko shakka babu idan Shugaban kasa ya saurare ni, shawarata ita ce ta gaggauta duba nadin da aka yiwa kwamishinonin zabe da Majalisar Dattawa ta amince da su kwanan nan.

Advertisement

“Yana da matukar muhimmanci, domin a fili, ba wai kawai tana aike da sakon da ba daidai ba game da aniyar gwamnati na inganta sahihin zabe, yana kuma nuna cewa, ka sani, akwai rashin ko in kula game da kare ‘yancin kai da nuna son kai na zaben hukumar gudanarwa.

“Zan so in yi imani cewa ko dai ba a yi wa Shugaban kasa bayani ba ko kuma ba a ba shi cikakkun bayanai game da wadannan nade-naden ba.”

Advertisement

A wani labarin kuma Ka Dakatar da Yin Murna Kamar Ronaldo’ – Dan Wasa Vidal Ya Soki Garnacho

Gwamnatin tarayya ta ce yanzu haka shirye-shirye sunyi nisa domin sauya akalar motoci har milyan 10 masu amfani da man fetir zuwa amfani da Gas nan da watanni 36 masu zuwa.

Advertisement

Karaminin ministan Mai, Ekperikpe Ekpo ne ya baiyana haka a yayin baje kolin mai da iskar gas na shekarar bana wanda ake gudanarwa a birnin Abu Dhabi na hadaddiyar daular larabawa.

A wata sanarwa da kakakinsa Louis Ibah ya fitar, ya baiyaan cewar a yanzu haka anyi kawance da kanfanoni masu zaman kansu domin kawo kayayyakin da za’a yi amfani dasu wajen sauya akalar motocin nan da watanni 9 masu zuwa.

Advertisement

Ya ce matakin wani yunkuri ne na inganta yin amfani da Gas a tsakanin motocin kasar a maimakon Man fetir da suka dogara dashi.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending