Connect with us

News

Ganduje ya na’da Farfesa Attahiru Jega A matsayin Shugaban Majalisar Gudanarwar Jami’ar Ilimi ta Sa’adatu Rimi.

Published

on

Gwamnan jihar Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya naɗa tsohon shugaban hukumar zaɓe mai zamanta ta ƙasa (INEC), Farfesa Attahiru Jega a matsayin shugaban zartarwa Shugaban Majalisar Gudanarwar Sa’adatu Rimi dake Kano.

Hakan na cikin wata sanarwa ce da Kwamishinan yaɗa labarai na jihar Kano kwamared Muhammad Garba ya fitar.

Advertisement

Kotu a Jigawa ta yanke hukunci kisa ta hanyar rataya kan wasu mutane 3

Sanarwa ce gwamna Ganduje ya kuma amince da naɗin Oba Dakta Sanata Moshood Olalekan Ishola Balogun na Aliiwo a matsayin babban uba kuma shugaban kwamitin gudanarwar Jami’ar ta Sa’adatu Rimi.

A cewar Muhammed Garba sauran mambobin kwamitin gudanarwar Jami’ar sun haɗa da: Dakta Muhammad Adamu Kwankwaso, Hajiya Zulaiha UM Ahmed, Dakta Ibrahim Yakubu Wunti, Dakta Halima Muhammad da kuma Alhaji Sabi’u Bako.

Advertisement

A baya-bayan nan ne dai hukumar kula da jami’o’i ta Nigeria (NUC), ta amince da ɗaga likkafar kwalejin ilimi ta Sa’adatu Rimi zuwa Jami’a.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending