Connect with us

News

Wani Dan Sanda Ya Mutu Yana Kokarin Raba Fada A Neja

Published

on

Wasu matasa sun kashe wani dan sanda da yake kokarin raba fada tsakanin wasu kungiyoyi da ba sa ga-maciji da juna a Karamar Hukumar Lavun ta Jihar Neja.

Dan sandan mai  sunan Nasiru, an kashe shi ne a kauyen Manima na gundumar Gaba da ke yankin.

Advertisement

Ganduje ya na’da Farfesa Attahiru Jega A matsayin Shugaban Majalisar Gudanarwar Jami’ar Ilimi ta Sa’adatu Rimi.

Wasu majiyoyi sun shaida wa Aminiya bayan barkewar rikicin, an gayyato jami’an tsaro, inda bayan zuwansu, sai mambobin kungiyoyin suka sare shi da makamai a ka.

Wani mazaunin yankin ya shaida wa wakilinmu cewa kafin faruwar lamarin, dan sandan ya halarci wani taron zama lafiya a kauyen Doko na Karamar Hukumar ta Lavun, inda aka tattauna batun yawan faruwar rikice-rikice kan filaye a yankin.

Advertisement

Ya ce, “Yanayin yadda ake yawan samun matsalar rikici tsakanin mutanen yankinmu a ’yan kwanakin nan abun takaici ne. Kuma galibi ana yi ne ko dai a kan filaye ko kuma sarautu.

“Ko gabanin kisan dan sandan, sai da ya halarci wani taron zaman lafiya a kauyen Doko, kafin rikicin ya barke a Manima, inda suka je su shiga tsakani.”

Advertisement

Da wakilinmu ya tuntubi Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar, DSP Wasiu Abiodun, ya ce tuni suka kama mutum biyu da ake zargi da hannu a lamarin.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending