Connect with us

News

Yajin Aikin NLC:Maganar soma yajin aiki ranar Litinin ƙarya ce – Nlc 

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI

 

Kungiyar Kwadago ta Najeriya NLC ta yi watsi da sanarwar yajin aikin da ake zargin ta shirya yi a ranar Litinin.

Benson Upah, shugaban yada labarai da hulda da jama’a na hukumar ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi a Abuja.

Kungiyar kwallon kafar Arsenal ta koma saman teburin firimiya bayan doke Brighton

Akwai wata sanarwa mai dauke da sa hannun babban sakataren kungiyar ta NLC da kuma babban sakataren kungiyar ta TUC, Emmanuel Ugboaja, da Nuhu Toro, dake cewa za a fara yajin aikin a fadin Najeriya ranar Litinin.

Premium Times ta cewa A cewar Upa, maganar karya ce kuma babu sanarwar yajin aiki daga gare su.

Advertisement

“Muna so mu sake tabbatar wa Ƴan Najeriya cewa wannan sanarwar ba ta fito daga gare mu ba, kuma ba mu da niyyar fara wani yajin aiki a wannan lokacin,” in ji shi.

Ya ce an shawarci ‘yan Najeriya da su ci gaba da hidimomin su yi watsi da sanarwar su dauke shi a matsayin na karya kawai.

A wani labarin kuma Kungiyar kwallon kafar Arsenal ta koma saman teburin firimiya bayan doke Brighton

Yanzu dai Babu wani Abu da al’ummar jihar kano ke yawan tattaunawa akansa Kamar batun shari’ar zaben gwamnan jihar.

Wakilin jaridar Inda Ranka Yasir Sani Abdullahi ya gano yadda kusan da yawa daga cikin wuraren zaman alumma da kasuwanni harma da ofisoshin gwamnatin da masu zaman Kansu, Babu wani batu da yafi daukar hankali Kamar batun shari’ar

Magoya bayan dukkan babgarorin manyan jam’iyyun APC Dana NNPP na bugar kirgin samun nasara a kotun koli.

Advertisement

Jam’iyyar APC na da kwarin guiwar cewa Zata Kara samun nasara a kotun koli kasancewar kotun farko da ta biyu duka ta Bata nasara

Sai dai jam’iyyar NNPP Bayan korafe korafe da tayi akan hukunce hukunce na kotun baya, yanzu ta bayyana kwarin guiwar da take dashi na samun nasara a kotun koli.

Al’ummar jihar kano da dukkan bangarorin manyan jam’iyyun APC Da NNPP na dakon hukuncin na karshe na kotun koli wadda ake saran Zata yanke cikin karshen watan Nan, shi zai kawo karshen jayayya da kowane bangare keyi a jihar kano.

Masu iya magana na cewa Shari’a mace ce da ciki ba’asan wa Zata Haifa ba.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending