News
Sojojin Najeriya sun kuɓutar da mutum 52 da aka yi garkuwa da su kamar Bayi a Sokoto
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Rundunar sojin Najeriya ta Hadarin Daji ta sake kuɓutar da mutum 52 da aka yi garkuwa da su a karamar hukumar Isa na jihar Sokoto.
Sanarwar da rundunar ta fitar, ta ce ta samu nasarar ceto mutanen ne a ranar Juma’a 22 ga watan Disamba, a ci gaba da samame da take yi a maɓoyar ƴan ta’addan.
Kisan-kai biyar da suka tayar da hankali a Arewacin Nijeriya a baya bayan nan
Sojojin sun ce sun kuma samu nasarar kashewa tare da lalata wuraren da ƴan ta’ddan a kauyukan Saruwa, Kubuta, Gundumi da kuma dajin Bunwanga da ke jihar ta Sokoto.
Mutanen da aka kuɓutar ɗin sun haɗa da maza 14, mata 32 da kuma yara guda biyu.
Dakarun sun ce za a duba lafiyar mutanen kafin miƙa su ga hukumomi domin su sake haɗuwa da iyalansu.
-
News3 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion7 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News3 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
