Connect with us

News

Sojojin Najeriya sun kuɓutar da mutum 52 da aka yi garkuwa da su kamar Bayi a Sokoto

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI

 

Rundunar sojin Najeriya ta Hadarin Daji ta sake kuɓutar da mutum 52 da aka yi garkuwa da su a karamar hukumar Isa na jihar Sokoto.

Sanarwar da rundunar ta fitar, ta ce ta samu nasarar ceto mutanen ne a ranar Juma’a 22 ga watan Disamba, a ci gaba da samame da take yi a maɓoyar ƴan ta’addan.

Kisan-kai biyar da suka tayar da hankali a Arewacin Nijeriya a baya bayan nan

Sojojin sun ce sun kuma samu nasarar kashewa tare da lalata wuraren da ƴan ta’ddan a kauyukan Saruwa, Kubuta, Gundumi da kuma dajin Bunwanga da ke jihar ta Sokoto.

Mutanen da aka kuɓutar ɗin sun haɗa da maza 14, mata 32 da kuma yara guda biyu.

Advertisement

Dakarun sun ce za a duba lafiyar mutanen kafin miƙa su ga hukumomi domin su sake haɗuwa da iyalansu.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending