Connect with us

News

Gwamnatin Tarayya Ta Baiwa Kowanne Gwamna Naira Biliyan 30 – Akpabio

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Shugaban Majalisar dattawan Najeriya, Godswill Akpabio yace gwamnatin tarayya ta bai wa kowannne gwamnan jiha naira biliyan 30 domin amfani da su wajen ragewa talakawa radadin tsadar rayuwar da suke fuskanta.

Advertisement

Akpabio ya bayyana haka ne lokacin zaman majalisar tarayyar, a ci gaba da tattauna irin halin kuncin da jama’ar kasar suka samu kan su a ciki, wanda ake dangantawa da cire tallafin mai.

Za,mu Fara hukunta ‘Yansandan da ke amfani da sunan IGP wajen aikata ba daidai ba.

Shugaban majalisar yace ya samu wadannan bayanai ne daga wajen hukumar tara kudaden haraji ta kasa da ake kira ‘Internal Revenue Services’ wadda ta mikawa jihohin wadannan kudaden da ake Magana a kan su.

Advertisement

 

Akpabio yace wadannan kudade sun saba da naira biliyan bib-biyu da aka bai wa gwamnonin daga cikin biliyan biyar-biyar na rancen samarwa jama’ar su tallafin rage radadin cire tallafin man fetur.

Advertisement

 

Shugaban majalisar ya bai wa gwamnonin shawara wajen yin amfani da wadannan makudan kudade ta hanyar da ta dace domin ganin jama’ar jihohin su sun samu tallafin da ya dace, musamman abinda ya shafi abinci.

Advertisement

 

Akpabio yace ana iya cimma nasarar gabatar da tallafin ne ta hanyar amfani da shugabannin kananan hukumomi saboda kusancin su da mutanen dake yankunan karkara.

Advertisement

 

Shugaban majalisar wanda ya yi watsi da zanga zangar da aka gani a wasu jihohin kasar da ake danganta su da tsadar rayuwa, ya zargi ‘yan adawa da daukar nauyin su, duk da kokarin da yace majalisar dattawan na yi domin tinkarar matsalar tare da gwamnatin tarayya.

Advertisement

 

Akpabio yace babu wani mahaifin dake fatar ganin ‘dan sa ya kwanta ba tare da ya ci abinci ba, saboda haka ya bukaci takwarorin sa da su mayar da hankali a kan daukar matakin samo abinci duk inda yake domin wadata jama’a.

Advertisement

Yanzu haka ‘yan Najeriya na ci gaba da cacakar shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu a kan yanayin da kasar ta samu kan ta, na hauhawan farashin kayan masarufi da kuma tsadar rayuwa, saboda abinda suka kira rashin shugabanci na gari.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending