News
Majalisar wakila ta yi yunkurin kara yawan tarar da ake ci kan wadanda aka samu da lefin wulakanta Tutar Najeriya
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Majalisar wakila na wai yunkuri domin kara yawan tarar da ake ci kan wadanda aka samu da lefin wulakanta Tutar Najeriya daga naira 100 zuwa naira dubu 100.
A jiya ne kudirin yin gyara kan girmama Tutar Najeriya ya tsallake karatu na biyu a zauren majalisar wakilan.
Akwai fursunoni da dama da ake tsare dasu a gidan yarin Kurmawa, Kano haka kawai
Dan majalisa Sada Soli na jam’iyyar APC daga jihar Katsina wanda ya gabatar da kudirin, ya ce ana samun daidaikun al’umma da kuma jama’ar gari da wasu kungiyoyin dake wulakanta tutar Najeriyar.
Da yake yanke hukunci kan kudirin, Mataimakin shugaban majalsiar Benjamin Kalu ya mika kudirin gaban kwamitin majalisar daya da ce domin daukar mataki na gaba.
-
News3 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion6 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News2 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
