Connect with us

News

Matashi Ya Banka Wuta A Masallaci Ana Tsaka Da Sallah A Kano

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Masallata da dama ne suka kone bayan wani matashi da har ya zuwa yanzu ba a gano wane ne ba ya yi amfani da fetur ya banka wuta a wani masallaci a Kano ana tsaka da Sallar Asuba.

Advertisement

Lamarin ya auku ne a kauyen Larabar Abasawa da ke karamar hukumar Gezawa ta Jihar Kano.

  1. UTME 2024: Hukumar JAMB ta saki ƙarin sakamako 36,540

Ko da ya zo ana tsaka da sallah sai ya kulle dukkanin kofofin masallacin, inda kafin masallatan su farga ya watsa fetur sannan ya cinna wuta ya tsere kamar yadda wani mazaunin garin ya shaida wa Aminiya.

Kafin mutanen waje su ankara su kawo masu dauki kimanin mutum 20 sun kone kuma take aka garzaya da su asibitin kwararru na Murtala Muhammad da ke birnin Kano.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending