Connect with us

News

Wani Gungun ‘Yan Ta’adda Sun Fille Kan Matasa 10 A Jihar Neja

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Wani gungun ‘yan ta’adda da aka fi zaton cewa mayakan kungiyar Boko Haram ne sun kashe a kalla mutane 20 a wasu hare-hare da suka kai a karamar hukumar Shiroro da Bassa da ke jihar Neja.

Bayan sun kai hari karamar hukumar Shiroro, ‘yan ta’addar sun sake kai wani harin a karamar hukumar Bassa inda suka kashe wasu matasa 10 ta hanyar fille musu kai.

Kylian Mbappe Zai Sa Riga Mai Lamba 9 A Sabuwar Kungiyarsa

Wasu shaidun gani da ido da suka bukaci a boye sunansu sun shaidawa Rfi Hausa cewa ‘yan ta’addar sun kashe matasan ne saboda sun ki amincewa da tayin su shiga kungiyar Boko Haram.

Wani mazaunin yankin da ya samu damar tserewa yayin harin ya shaidawa Rfi din cewa ‘yan ta’addar sun tilastawa wasu mutanen yankin rike kawunan matasan tare da daukar su hoto.

Shaidun sun bayyana cewa ‘yan ta’addar sun kai hari garin da tsakar ranar Alhamis tare da daukan lokaci suna cin karensu babu babbaka ba tare da shakkar komai ba.

Advertisement

Rfi Hausa ta rawaito cewa majiyarta ta shaida mata cewa ‘yan ta’addar sun ware mutum 20 daga cikin mutanen da suka tattara tare da yi musu kisan gilla.

Wannan sabon harin na zuwa ne wata biyu cif-cif bayan wasu ‘yan ta’addar sun kai hari kauyen Allawa a karamar hukumar Shiroro inda suka fillewa wasu mutane tara kai.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending