Connect with us

News

Shugaban Kasar Tunisiya Ya Kori Minista Kan Mutuwar Mahajjata 

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

Shugaba Kais Saied na Tunisiya, ya tsige ministan harkokin addinin kasar daga mukaminsa sakamakon mutuwar mahajjatan kasar 49 a Saudiya saboda tsananin zafi.

Kamfanin dillancin labaran kasar, TAP ya ruwaito cewa, Shugaba Saied ya kori Ibrahim Chaibi daga mukaminsa ba tare da wani karin bayani ba. Tuni dai Chaibi ya dauki alhakin yin sakaci a wajen sanya ido kan mahajjartan. Sai dai a cewarsa, alhazan kasar 44 daga cikin wadanda suka gamu da ajalin nasu a kasa mai tsarki, ba su yi rijistan aikin hajji ba, inda sun tafi sauke faralin ne da takadar Visar yawon bude ido.

Advertisement

Wasu Sojoji Sun Lakada Wa Wani Sufeton ‘Yan Sanda Dukan Tsiya Har Lahira 

Hukumomin Saudi Arabiyya na cewa, yawancin mahajjatan da suka rasa rayukansu sakamakon tsanannin zafi ba su yi rijistar aikin hajji ba, wanda ya ke da matukar wuya a iya tantance adadin su ko ma gano su.

A gefe guda, gwamnatin Masar na shirin kwace lasisi tare da hukunta kamfanoni 16 da suka shirya jigilar aikin hajji bana ba bisa ka’ida ba, yayin da ake zargin yawancin wadanda suka mutu a bana, sun fito ne daga Masar.

Advertisement

 

 

Advertisement

Dw

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending