Connect with us

News

Jami’ar KWASU Tayi Rangwamen N100,000 Ga Dalibai Masu Bukata Ta Musamman

Published

on

HausaKWASU ta rage N100,000 daga kudin makaranta ga dalibai masu bukata ta musamman

DAGA NUSAIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA 

Jami’ar Jihar Kwara (KWASU) ta sanar da rangwamen Naira 100,000 daga kudin makaranta ga dalibai masu bukata ta musamman, a wani yunƙuri na tallafawa rayuwarsu da sauƙaƙa musu samun ilimi.

Advertisement

Mataimakin shugaban jami’ar, Farfesa Shaykh-Luqman Jimoh, ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da mukaddashin daraktar hulɗa da jami’ar, Dr. Saidat Aliyu, ta fitar.

Kano Da Katsina, Sun Zama Sahun Gaba Wajen Matsalar Rashin Isassun Takardun Kudi

Hakazalika, Farfesa Jimoh ya ce jami’ar ta fara bayar da tallafin Naira 50,000 a kowane wata ga ma’aikatan makarantar masu fama da bukata ta musamman. Har ila yau, an ware guraben aikin koyarwa don masu bukata ta musamman a jami’ar.

Advertisement

Jimoh ya yi wannan bayani ne yayin taron bikin Ranar Masu Bukata Ta Musamman ta Duniya ta 2024, wanda aka shirya a ofishin tallafawa nakasassu da ke Sashen Ilimi na Musamman a jami’ar.

A cewar sa, wasu matakan da jami’ar ta ɗauka sun haɗa da; Samar da wakilci ga dalibai masu bukata ta musamman a ƙungiyar dalibai ta makarantar hadi da kafa ofishin tallafawa masu bukata ta musamman a jami’ar.

Advertisement

Farfesa Jimoh ya jaddada muhimmancin bayar da dama ga masu bukata ta musamman don su taka rawa wajen bunƙasa tattalin arziki. Ya kuma yi kira ga gwamnati da malaman jami’a su samar da sababbin dabaru da hanyoyin kawar da ƙalubalen da suke fuskanta a rayuwarsu.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending