News
Gwamna Na Shirin Sayar Da Man Fetur A Jihar Sa Kan N600 Duk Lita
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya sanar da cewa gwamnatin jihar za ta rage farashin man fetur ga manoma a yankunan da rikicin Boko Haram ya shafa.
Zulum ya sanar da wannan tallafi ne a jiya Juma’a a garin Bama yayin da ya kaddamar da rabon kayan noma ga manoma sama da 5,000 da Boko Haram ta taba korar su daga muhallansu.
Ana Zargin Amarya Da Zuba Guba A Abincin Liyafar Aurenta A Jigawa
A cewar gwamnan, farashin litar man fetur da ake sayarwa tsakanin N1,000 zuwa N1,200 a Maiduguri za a sayar wa manoma kan N600.
Wannan mataki, a cewar sa, na da nufin rage nauyin kudin da ke kan manoman a yankunan da su ka fuskanci lalacewar tattalin arziki da gine-gine sakamakon shekaru na rikici.
-
News3 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion7 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News3 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
