Connect with us

News

Kwamitin Majalisa Ya Bukaci Dakatar Da Sanata Natasha Na Tsawon Watanni 6

Published

on

Natasha

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Kwamitin ladabtarwa na majalisar dattawa ya bayar da shawarar dakatar da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan na tsawon watanni 6, biyo bayan dambarwar da ta barke tsakaninta da shugaban majalisar, Sanata Godswill Akpabio.

Advertisement

Tashar talabijin ta Arise TV ce ta rawaito wannan labari a yau Alhamis.

Kuskure Ne Fara Cin Abinci Tun Daga Gida Kafin Fara Tafiya Ga Mai Ajiye Azumin Ramadan – Sheikh Pantami

Ana dai alakanta wannan rikici da zargin da Sanata Natasha ta yi na cewa shugaban majalisar na kokarin yin lalata da ita, zargi da ya janyo cece-kuce a tsakanin bangarorin biyu.

Advertisement

Idan za a iya tunawa, a jiya Laraba wata kotun tarayya dake Abuja ta dakatar da majalisar dattawa daga daukar matakin ladabtawa akan Sanata Natasha, har sai an kammala sauraron karar da ta shigar a gaban kotu.

Har yanzu dai ana jiran jin matsayar majalisar game da wannan shawara da kwamitin ya bayar.

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending