News
Wani Saurayi Yayi Ajalin Budurwarsa Da Ke Shekarar Karshe A Jami’a
Rundunar ƴan sandan Jihar Ondo ta tabbatar da kisan da aka yi wa wata ɗaliba da ke shekarar ƙarshe a Jami’ar Adekunle Ajasin da ke Akungba-Akoko AAUA.
Mai magana da yawun rundunar, DSP Olayinka Ayanlade, ya shaidawa Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya NAN a ranar Asabar cewa ana zargin saurayin ɗalibar ne da kashe ta.
An Gano Wani Asibiti Da Ake Amfani Da Shi Wajen Sayar Da Jarirai
Ya bayyana cewa an kama mai gidan saurayin da wasu mutane da ake zargin sun taimaka wajen aikata kisan.
DSP Ayanlade, wanda bai bayyana sunan ɗalibar ba, ya ce ba’a kai ga kama saurayin da ake zargi da kisan ba.
NAN ta ruwaito cewa lamarin ya haddasa zanga-zangar lumana daga ɗaliban jami’ar a garin, inda suka tare hanyoyi da ababen hawa.
Sai dai mai magana da yawun rundunar ya ce ƴan sanda sun gana da masu zanga-zanga, kuma ankai ga dawo da zaman lafiya a yankin.
Da yake mayar da martani kan kisan, Shugaban Ƙungiyar Dalibai na AAUA, Mista Akeem Salami, ya yi Allah-wadai da yadda ake yawan kashe ɗaliban jami’ar ba gaira ba dalili.
Ya bayyana cewa bayan bincike an gano cewa an soka wa ɗalibar wuƙa har ta mutu, kuma aka bar gawarta a ɗakin saurayin fiye da kwanaki uku.
Shugaban SUG ɗin ya roƙi gwamnatin jihar, rundunar ƴan sanda da sauran hukumomin tsaro da su ɗauki matakin daƙile irin wannan kisan gilla da ke faruwa akai-akai a cikin jami’ar.
