Connect with us

News

Jami’an Tsaro Sama da 130 Sun Rasa Rayukansu A Katsina

Published

on

Gwamnatin Jihar Katsina ta bayyana cewa fiye da jami’ai 100 na Community Watch Corps, da ’yan sanda 30 sun mutu a yaƙi da ’yan bindiga.

Kwamishinan Tsaron Cikin Gida, Dr. Nasir Muazu, ya bayyana haka, yana mai ƙaryata rahotannin dake yaɗuwa a kafafen sada zumunta.

Advertisement

Kotu Ta Umarci NYSC Ta Bawa Mata Damar Sanya Siket

Ya ce wasu na ƙoƙarin haddasa fargaba da tayar da hankali ta hanyar yaɗa bayanan ƙarya kan halin da tsaro yake ciki a jihar Katsina.

Dr. Muazu ya ce tun bayan hawan Gwamna Dikko Radda a 2023, an sami ci gaba a yaƙi da ‘yan bindiga a yankuna da dama.

Advertisement

Ya lissafa ƙananan hukumomi 11 da suka fi samun sauƙin hare-hare, ciki har da Jibia, Katsina, Bindawa da Kafur, yayin da ƙananan hukumomi 4 ke fama da harin.

Kwamishinan ya ce Gwamna Raɗɗa na jajircewa kan tsaro, yana karɓar rahoto daga manyan jami’an tsaro duk da raunin da ya samu.

Advertisement

 

 

Advertisement

WIKKI TIMES

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending