News
Akalla Mutane Hudu Ne Suka Rasu Bayan Da Hilux Ta Yi Karo Da Tankar Gas A Kaduna
Akalla mutane hudu ne suka mutu a wani mummunan hatsarin mota da ya faru da yammacin Lahadi a kan babban titin Kaduna–Abuja, kusa da Kakau, Gonin Gora, a jihar Kaduna.
Hukumar Kiyaye Hadura ta Ƙasa (FRSC), reshen jihar Kaduna, ta tabbatar da faruwar hatsarin. Kwamandan FRSC na jihar, Iliyasu Tijjani, ya bayyana cewa hatsarin ya faru ne da misalin ƙarfe 4:30 na yamma, lokacin da motar Hilux mai saurin gaske ta yi karo da tankar gas.
Mutuwar Tsohon Sojan Nijeriya Ta Tilasta Jirgin British Airways Saukar Gaggawa A Barcelona
“Binciken farko ya nuna cewa gudu fiye da ƙa’ida da gangancin wucewa sune manyan abubuwan da suka haddasa hatsarin,” in ji Tijjani.
A cewar FRSC, mutane biyar ne ke cikin motar Hilux – maza hudu da mace ɗaya. Duk maza hudu sun mutu a Asibitin St. Gerard Catholic, yayin da mace ɗaya ke samun kulawa a Asibitin FRSC, Tollgate, Kaduna.
Karo ya lalata motar Hilux sosai, sannan ya janyo cunkoson ababen hawa na ɗan lokaci kafin jami’an ceto su isa wurin.
Kwamandan ya yi kira ga direbobi da su guji gudu fiye da ƙa’ida da gangancin wucewa, yana mai jaddada cewa mafi yawan hatsarurrukan da ke faruwa a titin Kaduna–Abuja na faruwa ne saboda rashin haƙuri da take dokokin zirga-zirga.
