Connect with us

News

Fadar shugaban kasa ta karyata labarin cewa an yi yunkurin sakawa Tinubu guba a abinci

Published

on

Tinubu Bola 750x430

Fadar shugaban ƙasa ya karyata jita-jitar da ke yawo a kafafen sada zumunta cewa an kama wasu ma’aikatan fadar bisa zargin yunƙurin saka guba a abincin shugaba Bola Ahmed Tinubu.

A cikin wata sanarwa da ya wallafa, Bayo Onanuga, mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin yaɗa labarai, ya bayyana cewa babu gaskiya a rahotannin da ke cewa an kama ma’aikatan da ke aiki a ɗakin dafa abinci na fadar.

Advertisement

Ɗakin Otal Da Kudin Kwana Daya Kai Kusan Miliyan 130 A Dubai

Sanarwar ta biyo bayan wani bidiyo da ya karade kafafen sada zumunta, inda ake ikirarin cewa jami’an tsaro sun cafke wasu ma’aikatan bisa wani shiri na saka guba.

Advertisement

Bidiyon ya jawo ce-ce-ku-ce a tsakanin jama’a kafin fadar shugaban ƙasar ta fito ta yi bayani.

Onanuga ya buƙaci al’umma da su guji yaɗa labaran da ba a tabbatar da su ba, yana mai jaddada muhimmancin tantance sahihancin labari daga majiyoyin hukuma kafin a yaɗa.

Advertisement

 

Premier Radio 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending