Connect with us

News

Trump Ya Ce Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Da Iran Ta Rushe

Published

on

Trump 768x501

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya ce yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Amurka da Iran ta rushe bayan sabbin hare-haren da ɓangarorin biyu suka kai wa juna.

Trump ya bayyana hakan ne yayin da yake magana da manema labarai a gefen taron ƙasashen NATO da aka gudanar a Ankara ranar Laraba.

Jami’an Ƴansanda Sun Kama Wani Sufeton Bogi  ‎

Ya ƙara da cewa ba ya son ci gaba da mu’amala da Iran, yana mai bayyana tattaunawa da ƙasar a matsayin “ɓata lokaci.”

Trump ya kuma yi kalamai masu zafi kan shugabannin Iran, yana mai cewa ba ya ganin wata fa’ida a ci gaba da yin hulɗa da su.

Kalaman na Trump na zuwa ne bayan Iran da Amurka sun yi musayar hare-hare tare da zargin juna da karya yarjejeniyar tsagaita wutar da aka cimma a baya, lamarin da ya sake ƙara tayar da hankalin rikicin da ke tsakanin ƙasashen biyu.

Advertisement

 

 

BBC 

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending