News
Trump Ya Ce Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Da Iran Ta Rushe
Shugaban Amurka, Donald Trump, ya ce yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Amurka da Iran ta rushe bayan sabbin hare-haren da ɓangarorin biyu suka kai wa juna.
Trump ya bayyana hakan ne yayin da yake magana da manema labarai a gefen taron ƙasashen NATO da aka gudanar a Ankara ranar Laraba.
Jami’an Ƴansanda Sun Kama Wani Sufeton Bogi
Ya ƙara da cewa ba ya son ci gaba da mu’amala da Iran, yana mai bayyana tattaunawa da ƙasar a matsayin “ɓata lokaci.”
Trump ya kuma yi kalamai masu zafi kan shugabannin Iran, yana mai cewa ba ya ganin wata fa’ida a ci gaba da yin hulɗa da su.
Kalaman na Trump na zuwa ne bayan Iran da Amurka sun yi musayar hare-hare tare da zargin juna da karya yarjejeniyar tsagaita wutar da aka cimma a baya, lamarin da ya sake ƙara tayar da hankalin rikicin da ke tsakanin ƙasashen biyu.
-
News1 day ago
Hukumar Kula Da Harkokin Shari’a Ta Tilasta Wa Alƙali Ritaya Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Naira 250,000 A Kano
-
News2 days ago
Jigawa: Sama da Gine-gine 200 Sun Lalace Sakamakon Iska Da Ruwan Sama Mai Ƙarfi
-
News2 days ago
Wasu Fusatattun Matasa Sun Hallaka Wani Mutum Tare Da Kona Gawarsa Kan Zargin Satar Babur A Kano
