News
“Rikicin ’Yan El-rufai: Bashir Ya Ce Bello Ba Zai Iya Yi Masa Komai Ba”
Ɗan tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, Bashir El-Rufai, ya ce yana kwana da wuƙaƙe da bindigogi, yana mai cewa ɗan uwansa kuma ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Kaduna ta Arewa, Bello El-Rufai, ba zai iya yi masa komai ba.
Bashir ya bayyana hakan ne a wani jerin rubuce-rubuce da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Asabar, inda yake sukar ɗan uwansa kan wasu batutuwan siyasa da na iyali. Daga baya ya goge wasu daga cikin rubuce-rubucen, waɗanda tuni suka yaɗu a kafafen sada zumunta.
Shugaba Tinubu Ya Nemi Kotun Amurka Ta Hana FBI Da DEA Fitar Da Bayanansa
A cikin rubuce-rubucen nasa, Bashir ya soki alaƙar siyasar Bello da Gwamnan Kaduna, Uba Sani, yana mai nuna rashin amincewarsa da yadda ɗan uwansa ke gudanar da harkokin siyasarsa a baya-bayan nan.
Bashir ya kuma yi wasu zarge-zarge kan Bello, ciki har da cewa ya fi mayar da hankali kan shan barasa da amfani da hodar iblis maimakon wakiltar al’ummar Kaduna ta Arewa da suka zaɓe shi a Majalisar Wakilai.
Sai dai waɗannan zarge-zarge da Bashir ya yi ba su samu tabbaci daga wata majiya mai zaman kanta ba, yayin da Bello El-Rufai bai fito fili ya mayar da martani kan zarge-zargen ba a lokacin da rahotannin suka bayyana.
Rikicin ya jawo ce-ce-ku-ce sosai a kafafen sada zumunta, musamman ganin cewa ’yan’uwan biyu ’ya’yan tsohon gwamnan Kaduna ne, kuma lamarin ya sauya daga sabanin siyasa zuwa musayar kalamai masu zafi tsakanin ’yan uwa.
-
News2 days ago
Jami’an Ƴansanda Sun Cafke Mai Safarar Makamai, Sun Kwato Harsasai 637 A Kaduna
-
News5 days ago
Pantami Da Yaransa Sun Fantama Min Ƙarya, Domin Babu Inda Na Ba Shi Haƙuri, Inji Hajiya Naja’atu Muhammad
-
News3 days ago
Jami’an NSCDC Sun Cafke Mutane Biyu Da Saniyar Da Ake Zargin Ta Sata Ce A Kano
