Connect with us

News

Kotu Ta Tura Mutane 28 Gidan Gyaran Hali Bisa Laifin Dukan Jami’in Dan Sanda A Kano

Published

on

kotu

Kotun Shari’ar Musulunci ta Ungogo, ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a Muhammad Shurama, ta tura wasu mutane gidan gyaran hali bisa zargin haɗa baki wajen tayar da hankalin al’umma, jikkata jami’in ’yan sanda da kuma hana jami’an tsaro gudanar da aikinsu.

Advertisements
Advertisements

Ƙunshin tuhumar ya bayyana cewa lamarin ya faru ne a garin Ɗan Kunkuru da ke Ƙaramar Hukumar Ungogo, inda ake zargin wasu matasa da tayar da hargitsi.

Advertisements

Jami’an Kwastam Sun Kama Dabbobi Sama Da 40 Da Aka Yi Safarar Su Ba Bisa Ka’ida Ba A Kano

Advertisements
Advertisements

Bayan da ’yan sanda suka isa wurin domin shawo kan lamarin, an kama mutane 28, yayin da wani jami’in ’yan sanda ya samu rauni.

Kotun ta tura waɗanda ake zargin gidan gyaran hali, inda ta sanya ranar 1 ga watan gobe domin sake gabatar da su da ci gaba da sauraron shari’ar.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending