News
Buhari ya yi jaje kan mutuwar sojojin saman Najeriya
Daga Muhammad Muhammad zahraddin
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya yi jajen mutuwar sojojin Najeriya biyu wadanda suka yi hatsarin jirgin saman soji a Kaduna da ke arewacin kasar.
A wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasar, Mallam Garba Shehu, ya fitar ya ambato Shugaba Buhari yana bayyana “damuwarsa” bisa mutuwar Flight Laftanar Abubakar Alkali da Flight Laftanar Elijah Haruna Karatu.
“Na yi matukar kaduwar da ba zan iya cewa komai ba bisa rasuwar wadannan matasa biyu wadanda suka sadaukar da rayuwar wajne bauta wa kasa,” in ji Buhari.
Ranar Talata ne jirgin rundunar sojin sama ta Najeriya ya yi hatsari inda duka jami’an biyu da ke cikinsa suka mutu.
A cikin shekara guda da ta gabata dai, jiragen sojin saman Najeriya na yawan faduwa, lamarin da ke sanadiyar mutuwar jami’an sojin.
-
News2 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion6 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News2 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
