News
Majalisar dokoki ta dakatar da ciyamomin Ƙananan Hukumomi 2 a Kaduna
Daga Muhammad Muhammad zahraddin
Majalisar dokokin Jihar Kaduna ta dakatar da wasu shugabannin kananan hukumomi guda biyu saboda zargin kashe kudade babisa ka’ida ba.
Shugabannin kananan hukumomin su ne Salasi Musa shugaban karamar hukumar Chikun da Abubakar Lawal na karamar hukumar Giwa.
Direbobin Uber da Bolt sun yi zanga-zanga a Abuja
Dan majalisar dake wakiltar Zaria Kewaye Alhaji Ahmed Chokali ya gabatar da kudirin dakatar da shugabannin biyu yayin zaman majalisar.
Ya ce majalisar ba za ta lamunci yanda mutanen ke karya ka’idojin gudanar da kananan hukumomi ba don haka za ta gudanar da bincike akansu.
Nan take shugaban Majalisar, Alhaji Yusuf Zailani ya umarci kwamatin kula da kananan hukumomi na majalisar ya gudanar da bincike tare da gabatar da rahotansa ga ‘yan majalisa.
-
News3 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion7 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News3 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
